WAƘA TA 119
Wajibi Ne Mu Kasance da Bangaskiya
(Ibraniyawa 10:38, 39)
-
1. A dā Allah yana aika saƙo
Ta wurin annabawansa.
Yau ta bakin Yesu Kristi, ya ce:
‘Mutane ku bauta min.’
(AMSHI)
In muna da bangaskiya,
Za ta sa mu sami ceto.
In mun nuna bangaskiya
Za mu yi rayuwa har abada.
-
2. Yesu Almasihu ya ce mana
Mu yi wa’azi da ƙwazo.
Muna wa’azin nan babu tsoro
Ga dukan maƙwabtanmu.
(AMSHI)
In muna da bangaskiya,
Za ta sa mu sami ceto.
In mun nuna bangaskiya
Za mu yi rayuwa har abada.
-
3. Nuna bangaskiya na kāre mu,
Za ta hana mu jin tsoro.
Muna jimrewa don mun san cewa
Cetonmu ya yi kusa.
(AMSHI)
In muna da bangaskiya,
Za ta sa mu sami ceto.
In mun nuna bangaskiya
Za mu yi rayuwa har abada.
(Ka kuma duba Rom. 10:10; Afis. 3:12; Ibran. 11:6; 1 Yoh. 5:4.)