Hausa
Me Ya Sa Shaidun Jehobah Su Ke Zuwa Ƙofa Ƙofa?
https://cms-imgp.jw-cdn.org/img/p/502012464/univ/art/502012464_univ_sqr_xl.jpg
ijwfq talifi na 1

Me Ya Sa Shaidun Jehobah Suke Zuwa Ƙofa Ƙofa?

Me Ya Sa Shaidun Jehobah Suke Zuwa Ƙofa Ƙofa?

 Yesu ya gaya wa mabiyansa su “almajirtarda dukan al’ummai.” (Matta 28:19, 20) Lokacin da ya aiki almajiransa na farko, Yesu ya gaya musu su je gidajen mutane. (Matta 10:7, 11-13) Bayan mutuwar Yesu, Kiristoci na ƙarni na farko sun ci gaba da baza saƙonsu ‘gida gida da kuma a sarari.’ (Ayyukan Manzanni 5:42; 20:20) Muna bin misalin waɗancan Kiristoci na farkon kuma mun ga cewa za mu fi saduwa da mutane ta wurin hidimar ƙofa ƙofa.