TAMBAYA TA 1
Wane ne Allah?
“Bari mutane su san cewa kai wanda sunanka Jehobah ne, kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a dukan duniya.”
Zabura 83:18
“Ku san cewa Jehobah Allah ne. Shi ne ya yi mu, mu kuwa nasa ne.”
Zabura 100:3
“Ni ne Jehobah. Sunana ke nan; ba na ba wa kowa ɗaukakata, ko in ba wa siffofi yabon da ya kamata a ba ni.”
Ishaya 42:8
“Duk wanda ya kira ga sunan Jehobah zai sami ceto.”
“Hakika, kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma Allah ne ya gina kome.”
“Ku ta da idanunku sama ku duba. Wane ne ya halicci abubuwan nan? Shi ne Wanda yake musu ja-goranci kamar sojoji, ya san yawansu; yana kiran kowannensu da sunansa. Saboda yawan ƙarfinsa da ikonsa mai ban mamaki, babu ko ɗayansu da ya ɓata.”
Ishaya 40:26

