Littafi Mai Tsarki—Fassarar Sabuwar Duniya

Me Zai Taimaka Maka Ka Zama Mai Farin Ciki?

Hausa
Me Zai Taimaka Maka Ka Zama Mai Farin Ciki?
https://cms-imgp.jw-cdn.org/img/p/1001061100/univ/wpub/1001061100_univ_sqr_xl.jpg
nwt pp. 26-27

TAMBAYA TA 15

Me Zai Taimaka Maka Ka Zama Mai Farin Ciki?

“Gwamma a ci abinci kaɗan a wurin da akwai ƙauna, da a ci naman bijimi mai ƙiba a wurin da akwai ƙiyayya.”

Karin Magana 15:17

“Ni Jehobah, ni ne Allahnku, Wanda yake koya muku don ku amfana, Wanda yake nuna muku hanyar da za ku bi.”

Ishaya 48:17

“Waɗanda suka san cewa suna bukatar ja-gorancin Allah, suna farin ciki, domin Mulkin sama nasu ne.”

Matiyu 5:3

“Dole ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.”

Matiyu 22:39

“Abin da kuke so mutane su yi muku, ku ma ku yi musu hakan.”

Luka 6:31

“Masu farin ciki ne waɗanda suke jin kalmar Allah, kuma suke aikata ta!”

Luka 11:28

“Ko da mutum yana da dukiya da yawa, ba za su ba shi rai ba.”

Luka 12:15

“Saboda haka, idan muna da abin da za mu ci da rigunan sakawa, za mu gamsu da waɗannan abubuwa.”

1 Timoti 6:8

“Bayarwa tana sa farin ciki fiye da karɓa.”

Ayyukan Manzanni 20:35